Daga Masnus panda : TABBAS BIRI YAYI KAMA DA MUTUM

TABBAS BIRI YAYI KAMA DA MUTUM

Wallahi Aliyu Sani madaki Mai gaskiya ne, Mai sauraro Bari kaji Abin da ya faru tsakanin madaki da Rabiu Bichi a INEC.

A lokacin da uwar jam,iyar P.D.P ta jahar Kano ta zabi Rep. Aliyu Sani madaki da shugaban jam,iya Rabiu suleman Bichi ta Turasu hukumar Zabe wato INEC su sa ido a matsayin su na wakilan jam,iyar P.D.P.

Amma mutumin naka shi Rabiu kenan Yana ji Yana gani hukumar Zabe take ta sokewa Engr Abba kabir Yusuf kuri,ar sa. Amma yayi shiru dake bakin su Daya Kuma ya karbi kudinsu yaci.

Shine fa Rep. Aliyu Sani madaki yaga Abin da yake faruwa yayi yawa, yafara yin magana Amma shi Rabiu Bichi yace yayi shiru ai nine shugaban jam,iya.

Takai Takawo har sa insa ta shiga tsakanin su da madaki shine madaki yayi zuciya ya fice daga wajen Ashe matumin naka haka yaso.

Fitar mai Daraja madaki ke da wuya kawai suka suke kuri,a sama da 40,000 Aka kirkiri Wai (Inconclusive).

Kaga kenan yaci Rabin kudi kimanin naira miliyan 250 saura Rabi.

Duk mu bamu gane ba sai yanzu da haka ta faru A

Daga Masnus panda : TABBAS BIRI YAYI KAMA DA MUTUM

TABBAS BIRI YAYI KAMA DA MUTUM

Wallahi Aliyu Sani madaki Mai gaskiya ne, Mai sauraro Bari kaji Abin da ya faru tsakanin madaki da Rabiu Bichi a INEC.

A lokacin da uwar jam,iyar P.D.P ta jahar Kano ta zabi Rep. Aliyu Sani madaki da shugaban jam,iya Rabiu suleman Bichi ta Turasu hukumar Zabe wato INEC su sa ido a matsayin su na wakilan jam,iyar P.D.P.

Amma mutumin naka shi Rabiu kenan Yana ji Yana gani hukumar Zabe take ta sokewa Engr Abba kabir Yusuf kuri,ar sa. Amma yayi shiru dake bakin su Daya Kuma ya karbi kudinsu yaci.

Shine fa Rep. Aliyu Sani madaki yaga Abin da yake faruwa yayi yawa, yafara yin magana Amma shi Rabiu Bichi yace yayi shiru ai nine shugaban jam,iya.

Takai Takawo har sa insa ta shiga tsakanin su da madaki shine madaki yayi zuciya ya fice daga wajen Ashe matumin naka haka yaso.

Fitar mai Daraja madaki ke da wuya kawai suka suke kuri,a sama da 40,000 Aka kirkiri Wai (Inconclusive).

Kaga kenan yaci Rabin kudi kimanin naira miliyan 250 saura Rabi.

Duk mu bamu gane ba sai yanzu da haka ta faru A

Daga malam yahuza mai daraja : yakamata jama’a suyi watsi da labarin da yake yawo akan Engr Abba k. Yusif

Yakamata jama’a suyi watsi da labarain da yake Yawo cewa Engr. Abba K. Yusuf yayi nasara a kotun koli. An buga labarin ne a ‘yan watannin da suka gabata lokacin da muka yi nasarar shari’armu da Alh. Al-amin Little.

A yanzu, duk wani bayani dangane da shari’ar Engr. Abba K. Yusuf zai fito ne daga ofishin me Magana da Yawun Engr. Abba K. Yusuf ko ofishin Jam’iyyar mu.ta p.D.P

Saboda haka, muna kara kira ga magoya bayan Jam’iyyar mu da kuma wadanda suke Mana Fatan Alkhari da su ci gaba da yin addu’ar samun nasarar Engr Abba K. Yusuf a kotun koli kan karar da ya shigar Na bayyana Ganduje a matsayin gwamnan jihar Kano.

Kamar yadda Kotun koli ke shirin fara sauraron gobe, muna fatan sanar da magoya bayanmu da masu Yimana kyakkyawan Fata cewa Kotu za ta yanke hukunci bayan ta saurara gobe ko kuma tana iya sanya Wata ranar Dan yanke hukunci.

Daga : Malam Yahuza Mai Daraja✍️

Ko kunsan yaren Hausa ne asalin yaren Misirawa a zamanin Fir’auna

Masana tarihi sun bayyana yaren Hausa a matsayin yaren da Misiriwan zamanin Fir’auna suka yi amfani dashi.

Bayan wani rahoto da sashin Hausa na rediyon DW ya fitar akan batun, rediyon ta tattauna da wani masanin tarihi dan kasar Nijar wanda ya tabbatar da ikirarin kasancewar yaren Hausa a matsayin yaren da mutanen zamanin Fir’auna suke yi.

Masanin tarihi, Sule Garba, ya kara da cewa mutanen zamanin Fir’auna sun fara rayuwarsu ne a kauyen ‘Dan Baki’ dake garin Damagaram na Jamhuriyar Nijar.

Hakan na zuwa ne bayan da aka gano wani ginin tubalin ‘Pyramid’ irin na kasar Misra, ginin da turawa, masana tarihi suka tabbatar da Misirawan da sukayi kaura zuwa kasar Misira ne suka ginashi. Kuma shine ginin ‘Pyramid na farko kafin su gina na kasar Misra.

Haka zalika ya tabbatar da cewa yaren da Misirawan zamanin Fira’auna sukeyi mai suna Hieroglyphs, Hausa ce ba wani abu ba. Domin babu wani yare da ake rubuta “RAna” da ma’anar Rana (Sun) take fitowa idan ba yaren Hausa ba.

DABO FM ta gudanar da binciken cewa an fara tabbatar da alakar Hausawa da Misirawan zamamin Fir’auna shekaru 200-300 da suka gabata.

A shekarar 1938, fitaccen marubuci Werner Vicychl, ya tabbatar da alaka a cikin wani littafi da ya wallafa.

Hukumar kyautata ilimi da kimiya da al’adu ta majalisar dinkin duniya ‘UNESCO’ ta tabbatar da alakar yaren Hausa da yaren Misirawan zamanin Fir’auna a wani littafi mai suna ‘The peopling of ancient Egypt and the deciphering of Meroitic script‘.

Binciken DABO FM ya kara lulubo wasu kalmomi da suke kara tabbatar da Hausa a matsayin Misirawan zamanin Fir’auna;

An gano daga cikin fassara da akayi a yaren Misirawan lokacin, Misirawa suna kiran Fir’auna da sunan kalmar ‘Saraki’ wanda har ila yau yana amfani da ita a kasar Hausa wajen kiran Sarki.

A cikin kalmomin yaren Fir’aunawa akwai ‘Tuta’ – wacce take da ma’ana daya da ta yaren Hausa da kalmar ‘Qasa’ da nufin Ƙasa da sauren dubban kalmomi.

Daga Nuraddeen M Hamdullahi MAGANAR DOLLARS AKWAI SABON TSALLE

.

Dama bahaushe yayi gaskiya duk Wanda yaci yadin mage to dole kuwa sai yayi amansa koda kuwa baya so.Kano garin shehu Usman Dan fodio garin shehunnan malamai masu daraja.kano garin jagoran talakawan Nigeria senator Rabiu Musa kwankwaso .Duk Wanda yaci kudin kanawa to kugaya Masa wlh bai ci bulus ba domin bayan tiya akwai watacaca

Zulum zai gina gidaje dubu 10 a manyan biranen Borno, zai rufe sansanin ‘yan gudun hijira a Maiduguri da Jere a 2020

Daga Babandi Garba Abadam 

Gwamnatin jihar Borno zata gina rukunin gidaje Dubu 10,000 a cikin manya manyan biranen jihar tare da hangen nesan sake maido da ‘yan gudun hijirar tare da rufe sansanonin’ yan gudun hijirar a cikin Maiduguri da Jere a shekara ta 2020. Gwamnan ya sanar da haka a wurin taron kaddamar da rawararren Rawar Ra5pid (RRS).

Zulum ya kuma sanar da cewa, an kuma samar da karin rukunin Gida Dubu 10,000 na Shugaba Buhari da za a gina a jihar.

“Na yi matukar farin ciki da jinjinawa na gaya wa ‘yan Najeriya cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya nuna alheri da karfin gwiwa ya amince da gina gidaje 10,000 a jihar Borno a matsayin wani bangare na ayyukan gwamnatin tarayya a kokarinmu na dawo da su.” Farfesa Zulum ya ce.

Gwamnan ya kaddamar da Rapid Response Squad (RRS) kuma ya mika motocin Patrol guda 70. Wannan taron ya faru ne a fadar Shehu da ke Maiduguri.

‘Yan wasan sun hada da Sojoji,’ yan sanda, rundunar tsaron farar hula da sauran sojoji, Civilan JTF, Mafarauta da kuma na Vigilantes.

Buguda kari, Zulum ya amince da gina makarantun aji guda 60 na makarantar Mega a ɗakunan tsoffin rukunin kamfanonin CGC na gine-ginen kamfanin, a Moramti gaban rukunin gidaje 1000. An bayyana hakan ne ga manema labarai lokacin da gwamnan ya ziyarci wurin da aka gina shi.

Gwamnan ya tattara ayyukansa a Jami’ar Jihar Borno, inda ya duba ayyukan ci gaba da ake na gina hanyoyi da magudanan ruwa da kuma wasu sabbin jami’o’i guda biyu a cikin makarantar.

Zulum Gwamna ne a kullum yake tunanin talakansa da yanda zai yi masa hidima.

Design a site like this with WordPress.com
Get started